Gwamnatin Tarayya Ta Ƙarfafa Manufar Fallasa Badakala A Tsarin Doka

top-news


Daga Maryam Jamilu Gambo 

Gwamnatin Tarayya ta ɗauki mataki mai muhimmanci wajen ƙarfafa ingancin manufar fallasa badakala ta hanyar haɓaka wani ƙuduri da za ya bayar da kariya ta doka ga masu fallasa badakala. Wannan matakin na nufin magance ƙalubalen da ke hana aiwatar da manufar yadda ya kamata tare da ƙarfafa mutane su rika fallasa cin hanci da rashawa da kuma rashin da'a a harkokin gwamnati.

A wajen wani taron wayar da kai kan aiwatar da manufar fallasa badakala a Najeriya, Ministan Kuɗi kuma Ministan Haɗaɗɗen Tattalin Arziki, Mr. Wale Edun, ya jaddada aniyar gwamnati wajen tabbatar da gaskiya, adalci, da aminci a mulki.

Ya bayyana cewa manufar ta riga ta nuna alamar nasara, inda aka samu nasarar dawo da manyan kuɗaɗe tun bayan kafuwarta a shekarar 2016.

Mr. Edun ya ƙara da cewa ana shirin gabatar da wannan ƙuduri a gaban Majalisar Dokoki ta Ƙasa, wanda zai samar da doka mai ƙarfi don kare masu fallasa badakala tare da tabbatar da cewa ana gudanar da bincike cikin sirri da sauri. Ya ce, gwamnatin shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu za ta tabbatar da cewa an aiwatar da manufar bisa ƙa'ida da doka don cimma gaskiya da adalci a mulki.

A cewarsa, an dawo da kuɗaɗe naira biliyan 83,019,178,375.86; dala miliyan 609,083,391.91; Yuro miliyan 5,494,743.71 tsakanin shekarar 2017 zuwa 2023 ta hanyar wannan manufa.

Duk da haka, ya ce akwai bukatar ƙarfafa ƴan Najeriya su rungumi wannan yaki da cin hanci da rashawa da kuma fallasa ɓarnar kuɗaɗen gwamnati.

Tun da farko a jawabin maraba, Sakatare Mai daki-daki na Ma'aikatar Kuɗi ta Tarayya, Mr. Okokon Ekanem Udo, ya bayyana cewa tun bayan kafuwar wannan manufa a watan Disamba na shekarar 2016, ta kasance wata muhimmin hanya wajen bankado munanan ayyuka a cikin hukumomin gwamnati da masu zaman kansu. Ya ce wannan manufa na da nufin ba wa ƴan ƙasa damar fallasa ɓarnar kuɗaɗen gwamnati da sauran ayyukan zamba ga hukumomin da suka dace, ta yadda za a iya kafa gaskiya da adalci a mulkin Najeriya.

Duk da haka, kamar yadda ya bayyana, wannan manufa ta gamu da wasu ƙalubale wajen aiwatar da ita. A farkon lokacin kaddamar da ita, ƴan Najeriya sun nuna sha’awa sosai kan shigar da wannan manufa, amma ana bukatar ƙara himma don ci gaba da janyo hankalin mutane da kuma tabbatar da ingantaccen aiwatar da ita.

A jawabin ta na rufe taro, Sakatariya a Ma'aikatar Kuɗi ta Tarayya, Mrs. Lydia Shehu Jafiya, ta jaddada muhimmancin ƙarfafa kariyar masu fallasa badakala tare da kare sirrin su. Ta ce wannan matakin zai ƙara jawo mutane su yi fito na fito da cin hanci da rashawa da kuma ba da gudunmawa wajen inganta mulkin ƙasa.

Wannan taron wayar da kan na yini ɗaya yana da taken: “Matsaloli, Kalubale da Hanyoyin Warwarewa”.

NNPC Advert